To improve Nigeria’s non-Oil exports, President Buhari appoint Governor Badaru to head Committee as Nigeria targets $30 Billion non-Oil Revenue
In order to restructure Nigerian economy, the Federal Government is targeting at least $30 billion revenue from non-oil sources; this will be an increase of $25billion from the current $5 billion.
Nigerian Export Promotion Council (NEPC) Director General Segun Awolowo announced the plan after the National Economic Council (NEC) meeting chaired by Vice – President Yemi Osinbajo at the Presidential Villa.
In order to actualize this dream, the Presidency has constituted a committee to come up with a concise action plan on how to drive non-oil exports based on the presentations and discussions at the Economic Council's meeting.
Awolowo said the objectives of zero oil plan is to add $150 billion to Nigeria foreign reserves in the next 10 years, create 500,000 jobs, lift 10 million Nigerians out of poverty and integrate each state of the federation into the export value chain.
The focus of the plan is on the export of the following crops: rice, wheat, corn, palm oil, rubber, hides and skin, sugar, soya beans and automotive parts among others, and the destination countries for Nigeria’s exports to include Netherlands, China, Iran, Germany, United Kingdom, France, Spain, Italy, India, Saudi Arabia, among others.
Other members of the committee are the Lagos State Governor Akinwunmi Ambode, Ebonyi State Governor Dave Umahi, Ministers of Industry, Trade & Investment, Agriculture & Rural Development, Power, Works & Housing, Transportation and Finance.
Other members are the (NEPC), NEPZA, NEXIM Bank, and the Central Bank of Nigeria (CBN).
The Committee is expected to submit an initial report by November.
**********************************************************************
Domin inganta Kuɗin Shiga daga ɓangarorin da ba na albarkatun mai ba, Shugaba Buhari ya naɗa Gwamna Badaru ya jagoranci Kwamiti da zai samo hanyar da za a tara Dala Biliyan Talatin daga ɓangarorin da ba na Mai ba
Domin sake fasalin tattalin arzikin Najeriya, gwamnatin tarayya ta ƙudurci aniyar samar da aƙalla Dala Biliyan 30 daga ɓangarorin da ba na albarkatun mai ba, wanda hakan zai samar da ƙarin Dala Biliyan 25 daga Dala Biliyan 5 da ake samu a halin yanzu.
Darekta Janar na Hukumar Bunƙasa Kayayyakin da ake fitar da su Ƙasashen Waje Segun Awolowo ne ya sanar da haka bayan kammala taron Majalisar Tattalin Arziki na Ƙasa wanda Mataimakin Shugaban Ƙasa Farfesa Yemi Osinbajo ya jagoranta a fadar Shugaban Ƙasa.
Domin cimma wannan burin, fadar ta Shugaban Ƙasa ta kafa wani Kwamiti da zai zaƙulo hanyoyin da za a samar da waɗannan kuɗaɗen shiga daga ɓangarorin da ba na albarkatun mai ba, bayan tattaunawa da muhawarori da aka yi yayin taron Majalisar Tattalin Arziki na Ƙasa.
Awolowo yace an kafa wannan Kwamiti ne a shirin da gwamnati ke yi na daina dogaro da kuɗaɗen shiga da take samu daga albarkatun man fetur da samar wa Najeriya ƙarin kuɗin asusun ƙasa da ƙasa na Dala Biliyan 150 nan da shekaru goma, samar da ayyukan yi ga mutum 500,000, fitar da ƴan Najeriya sama da Miliyan 10 daga ƙangin talauci da kuma baiwa duk wata Jiha damar fitar da kayayyakin da take sarrafawa zuwa Ƙasashen ƙetare.
Abinda wannan shiri ya sanya gaba shine fitar da kayayyakin masarufi da albarkatun gona da suka haɗa da shinkafa, alkama, masara, Kwakwa, roba, fatu da ƙiraga, sukari, waken soya da kayayyakin motoci da sauran su zuwa Ƙasashen da Najeriya take hulɗar kasuwanci da su irin Holland, Sin, Iran, Jamus, Ingila, Faransa, Andalus, Italiya, India, Saudi Arabia da sauran su.
Sauran Mambobin Kwamitin sun haɗa da gwamnonin Lagos da Ebonyi wato Akinwunmi Ambode, da Dave Umuahia, Ministocin Masana'antu, Cinikayya da Zuba Jari, Albarkatun Noma da Raya Karkara, Wuta, Ayyuka da Gidaje, Sufuri da Kuɗi.
Sauran sun haɗa da hukumomin NEPC, NEPZA, Bankin NEXIM, Babban Bankin Najeriya (CBN).
Ana sa ran Kwamitin zata miƙa rahoton ta na farko a watan Nuwamba mai zuwa.
Auwal D. Sankara (Fica),
Special Assistant to the Executive Governor of Jigawa State on New Media
(Mataimaki na Musamman ga Maigirma Gwamnan Jihar Jigawa a Sabbin Kafafen Sadarwa)
04/10/2017