Adsent

Wednesday, 28 September 2016

GWAMNA BADARU ABUBAKAR YA KAI ZIYARAR TA'AZIYYA GA IYALAN SEN. DANZOMO. .





Gwamna Muhammad Badaru Abubakar na Jihar Jigawa ya Halarci ziyarar ta'aziyya ga iyalan tsohon Sanatan Jigawa ta Arewa maso Yamma, Sanata Dalha Danzomo, a gidan sa dake Unguwar Hotoro, a jihar Kano.

Tsohon Sanatan wanda ya rasu a daren jiya an yi masa sutura a yau da binne shi kamar yadda Addinin Musulunci ya tanadar. Gwamna Muhammad Badaru yace tsohon Sanatan mai kishin ƙasa ne kuma gogaggen ɗan Siyasa wanda ya bautawa al'umarsa tuƙuru. Daga nan yayi masa addu'ar samun rahama, ya kuma baiwa iyalansa haƙurin jure rashin.

A wani labari makamancin wannan, Gwamna Muhammad Badaru ya kai ziyarar ta'aziyya ga iyalan tsohon Babban Mai Shari'a na Ƙasa, Mai Shari'a Dahiru Mustapha, wanda yayi rashin ƙanwarsa Hajiya Hafsatu Mustapha. Gwamnan yayi addu'ar Allah yayi mata rahama, ya kuma baiwa iyalanta haƙurin jure wannan Babban Rashi.

Auwal D. Sankara (Fica),
Special Assistant to the Executive Governor of Jigawa State on New Media

(Mataimaki na Musamman ga Maigirma Gwamnan Jihar Jigawa a Sabbin Kafafen Sadarwa)
28/09/2016

Tuesday, 27 September 2016

DAGA MAJALISSAR JIHAR JIGAWA.. Rahoton Isah Ramin Hudu.



Majalissar dokokin Jihar Jigawa ta amince da karin wa'adin watanni Shida ga Shugabannin Kwamitotin riko na kananan hukumomin Jihar 27, Shugaban majalisaar Hon. Idris Garba Jahun ne, ya sanarda hakan a zaman majalissar na yau bayan dawowarsu daga hutun Babbar Sallah.

Tunda farko dai Dan majalissar Dokokin jiha mai wakiltar Mazabar Kazaure Hon. Barr. Yusuf Gada wadda shine mataimakin bulaliyar majalissar ya gabatar da kudirin Karin wa'adin watanni Shidan, abisa tanadin Sashe na 7 na dokar kananan hukumomin jihar jigawa.
Daga nan kudirin yasamu goyon bayan Dan majalissa mai wakiltar Mazabar Bulangu, Hon. Abudullahi Muhammad Toyin.

Muna Adduar Allah Ya Kara Tayasu Riko. Ya Cigaba Da Taimakon Gwamnatin Muhammadu Badaru Abubakar (Kadimul Islam) Da Mataimakinsa Barr. Ibrahim Hassan Hadejia.

Monday, 26 September 2016

ZA'A KEWAYE DUKKANIN MAKARANTUN PRIMARY DA KANANAN MAKARANTUN SAKANDIRE NA JIHAR JIGAWA. Daga Yahya Salisu Gabari.



Hukumar ilmi a matakin farko ta jihar Jigawa tace tana shirye shiryen kewaye makarantun firamare da kananan makarantun sakandaren
jihar nan domin kare su daga cin kan iyaka, Shugaban hukumar Alhaji Salisu Zakar ya bada tabbacin haka a lokacin da shugabannin kwamitin kula da harkokin ilmi na makarantun Kafin Hausa Mallam Madori suka ziyarci ofishinsa.

Shugaban Yace gwamnatin jiha tana yin dukkan abinda ya dace wajen kyautata yanayin koyo da koyarwa a makarantun jihar nan, tare da
alkawarin duba bukatun da suka gabatar. Alhaji Salisu Zakar ya yaba da irin gudunmawar da kwamitocin kula da harkokin ilmi na makarantu ke bayarwa wajen hana cin iyakokin makarantu. Tunda farko dai wakilin shugaban kwamitin Alhaji Abubakar Hassan ya shaidawa shugaban
hukumar cewar sun kawo ziyarar ne domin neman gina musu karamar sikandaren Arabiyya a unguwar shagari, sakamakon yawan jama'a da yankin yake dashi.

Sunday, 25 September 2016

GWAMNA BADARU ABUBAKAR YA KAI ZIYARAR TA'AZIYYA KANYA BUBBA.


Maigirma Gwamnan Jihar Jigawa Alhaji Muhammad Badaru Abubakar (MON, mni) a yau ya tafi garin Kanya Babba dake Ƙaramar Hukumar Babura domin ta'aziyyar matasa goma sha biyu da suka rasa rayukansu.

Matasan sun rasu ne sanadiyyar haɗarin mota da ya rutsa dasu a hanyar su ta zuwa Jihar Legas, bayan Bikin Babban Sallah.

Gwamna Muhammad Badaru ya je ta'aziyyar ne a fadan Maigirma Hakimin Kanya Babba kuma Makaman Ringim Alhaji Muhammadu Ibrahim.

Gwamna Badaru yace rasa waɗannan matasa abun alhini ne, kuma ba wai rashi ne ga al'umar Kanya Babba ko Ƙaramar Hukumar Babura kaɗai, yace babban rashi ne ga ɗaukacin al'umar Jihar Jigawa.

Gwamnan yace yana kyautata zaton mamatan suna cikin rahama, saboda sun rasa rayukansu ne a madaidaiciyar hanya, ta neman halak.

Gwamna Badaru yayi addu'ar Allah ya jikan mamatan, ya kuma bawa waɗanda suka samu raunuka lafiya, ya kuma bawa iyalan mamatan haƙurin jure wannan Babban Rashi.

A jawabinsa, Maigirma, Makaman Ringim kuma Hakimin Kanya Babba Alhaji Muhammadu Ibrahim ya godewa Maigirma Gwamnan da wannan ziyarar ta'aziyyar da ya zo musu, inda yace wannan hali ne na Shugaban da ya damu da al'umar sa.

A nan Hakimin yayi addu'ar Allah ya maida Maigirma Gwamnan da ƴan tawagar sa gida lafiya, ya kuma basu ladan ta'aziyya.

Auwal D. Sankara (Fica),
Special Assistant to the Executive Governor of Jigawa State on New Media
(Mataimaki na Musamman ga Maigirma Gwamnan Jihar Jigawa a Sabbin Kafafen Sadarwa)
25/09/2016

Friday, 23 September 2016

WA KE DA ALHAKIN TSARE BISHIR DAUDA??? Daga Isah Ramin Hudu

Wa keda Alhakin Tsare Sakataren Kungiyar Muryar Talaka Comrade Bishir Dauda? Gwamnatin Jihar Katsina ce ko kuwa? Bishir Dauda wadda yayi fice a Harkokin Kungiyoyi musannan kungiyar Muryar Takaka wadda shine Sakatarenta na kasa, jiya muka samu labarin kamashi da jami'an tsaro sukayi bayan kama shugaban Social Media na katsina da akayi.

Kawo yanzu dai bamu samu labarin Dalilin da yasa aka kamashi ba,
Idan har tabbata Gwamnatin Jihar Katsina ce. To a wani Dalili?

Idan babu wani dalili, to yazama wajibi ku sako mana Abin mu
Madamar gwamnatin Katsina tayi biris da wannan kiranye.....
To fa ta kwana da samun caccaka daga 'ya'yan kungiyar Muryar Talaka a gidajen Radio da Jaridu da dukkan wata kafa da doka ta laminta.
Idan yaso ta tattara dukkan 'yan kungiyar Muryar Talaka a turasu gidan kaso.

#Free_Bishir_Dauda