Adsent

Tuesday, 11 October 2016

YAN’KASUWA NA HADEJIA SUN YABAWA GWAMNATIN SARDAUNA/SHETTIMA.. Daga Saifullahi Abbas Hadejia.



JIHAR JIGAWA, A NIGERIA
***

Hadaddiyar kungiyar yan’kasuwa ta Hadejia ta bayyana gamsuwa bisa kulawar da Gwamnatin jihar jigawa ta nuna sakamakon iftila’in da ya samesu a kwanakin baya, Shugaban kungiyar Malam Bawada Isa ne ya bayyana haka lokacin da ya jagoranci shugabannin sauran yan kasuwa zuwa ziyarar godiya ga sakataren zartarwa na hukumar bada agajin gaggawa na jihar Jigawa a ofishinsa.

Malam Bawada Isa ya ce hakan ya nuna yadda Gwamna Muhammadu Badaru Abubakar ya damu da jin dadin al’ummar wannan jiha, A nasa jawabin sakataren zartarwa na hukumar, Alhaji Yusuf Sani Babura yace a koda yaushe burin Gwamnati shine kyautata jin dadin al’umma. Alhaji Yusuf Sani ya ce hukumar ta tallafawa mutane da dama wadanda suka gamu da iftila’i a fannoni daban daban tare da yabawa yan kasuwar bisa wannan ziyarar. Gwamnatin Jihar Jigawa a karkashin Jagorancin Gwamna Badaru Abubakar ta dukufa ne wajen taimakon Al'ummarta, hakan ne yasa Gwamnan yake maida hankali wajen taimakawa masu kananan sana'oi domin dogaro da kai. 

Rahoto daga wakilin Tsinkaya
Saifullahi Abbas Hadejia
New Media Correspondent
11/10/2016

BANKIN ZENITH TA BAIWA GWAMNATIN JIHAR JIGAWA KYAUTAR MOTAR BAS MAI CIN MUTUM 16...

ZENITH BANK DONATES 16 SEATER BUS TO JIGAWA STATE GOVERNMENT..




Zenith Bank Nigeria Plc has adopted Dutse Model International School for its Educational Intervention Programme. The Bank Zonal Manager Alhaji Umar Ahmad stated this when he paid a Courtesy Visit to Governor Muhammad Badaru Abubakar at the Government House.
He explained that this year, the Bank supported ten (10) best students selected from the Jigawa State Public Schools with Two Hundred and Fifty Thousand Naira (N250, 000.00) each as scholarship grant, in an effort to encourage them in their educational pursuit.

Alhaji Umar Ahmad pointed out that in an effort to ease official mobility; the bank donated 16 Seater Bus to Jigawa State Government as part of their Corporate Social Responsibility.
Responding, Governor Muhammad Badaru Abubakar expressed his appreciation for the visit and also thanked the management of the bank for the gesture.

He noted that the Bank and the State Government have a long cordial relationship, while urging the bank to continue with the laudable efforts.


Bankin Zenith ta zaɓi makarantar Dutse Model International School domin gudanar da shirinta na tallafawa harkar ilimi. Manajan Shiyya na Bankin Alhaji Umar Ahmad shi ya bayyana haka a yayin da ya kawowa Maigirma Gwamnan Jihar Jigawa Alhaji Muhammad Badaru Abubakar ziyara a Gidan Gwamnati. Ya bayyana cewa, a wannan shekarar na 2016, Bankin ta zaƙulo hazikan Ɗaliban makarantun sakandare guda goma daga makarantun gwamnati dake Jihar Jigawa, inda ta tallafawa kowannensu da kuɗi Naira Dubu Ɗari Biyu Hamsin (N250, 000.00) domin ƙarfafa musu gwiwa a harkar karatunsu.

Alhaji Umar Ahmad ya nuna cewa domin rage wa bangaren gwamnatin wahalhalu ta ɓangaren sufuri ne, yasa bankin taga dacewar bayar da gudunmawar Mota ƙirar Bas mai cin mutum 16. A jawabinsa, Gwamna Muhammad Badaru ya bayyana farin cikin sa da wannan ziyara da suka kawo masa tare da yin godiya ga bankin da wannan gudunmawa da suka bayar. Ya nuna cewa Bankin da Gwamnatin Jihar Jigawa suna da kyakkyawar alaƙa tun baya, inda ya bukace su, su ci gaba da tabbatar da wannan alaƙa.

Auwal D. Sankara (Fica),
Special Assistant to the Executive Governor of Jigawa State on New Media
(Mataimaki na Musamman ga Maigirma Gwamnan Jihar Jigawa a Sabbin Kafafen Sadarwa)
11/10/2016

Monday, 10 October 2016

GWAMNATIN JIHAR JIGAWA ZATA HAƊA GWIWA DA KAMFANIN ƘASAR AFIRKA TA KUDU DOMIN SAMAR DA MEGAWAT 80 NA WUTAN LANTARKI




Gwamna Muhammad Badaru Abubakar yace makamashin wutan lantarki yana sa matuƙar tasiri wajen janyo ra'ayin masu zuba jari a Jihar.
Gwamnan ya bayyana haka ne, a yayin da ya karɓi baƙuncin Manajin Daraktan Kamfanin Nova Scotia na Ƙasar Afirka ta Kudu Mr. Amit Modi tare da tawagar sa a gidan Gwamnatin Jihar Jigawa, dake Dutse.

Yace gwamnatin sa ta zagaya sassa daban daban na duniya domin nemo masu zuba jari a Jihar, don haka ake buƙatar tabbataccen wutan lantarki.
Alhaji Badaru Abubakar yace samar da lantarki ta hasken rana zai zama wani madogara ga Jihar domin janyo ra'ayin masu zuba jari a Jihar.
Gwamnan ya kuma bayyana cewa tasirin da wutan lantarki yake da shi wajen samar da masana'antu ba zai misaltu ba, don haka yace shiri yayi nisa na ƙulla yarjejeniya da kamfanin.

A nasa ɓangaren, Mai Martaba Sarkin Dutse, Alhaji Nuhu Muhammad Sunusi, yabawa Gwamnan yayi a ƙoƙarin da yayi na samar da kyakkyawar muhalli ga masu zuba jari a cikin Jihar, inda yace wannan aikin zai taɓa al'uma kai tsaye.
Tun farko a nasa jawabin, Manajin Daraktan Kamfanin samar da wutan lantarki na Nova Scotia, Mr. Amit Modi yace sun kawo ziyarar ne domin sanar da Maigirma Gwamnan irin cigaban da aka samu na gudanar da aikin.
Yace aikin wanda zai samar da ƙarfin wuta mai Megawat 80, zai lashe zunzurutun kuɗi kimanin Dala Miliyan 150.

A yayin da yake gabatarwa Maigirma Gwamnan taswirar aikin, yace za a fara aikin ne a rubu'i na uku na shekara mai zuwa.
A ƙarshe, ya ziyarci Maigirma Gwamnan da ya kai ziyara ƙasar na Afirka ta Kudu domin gane wa idanuwansa makamancin wannan aikin da kamfanin ta gudanar.
Auwal D. Sankara (Fica),
Special Assistant to the Executive Governor of Jigawa State On New Media
(Mataimaki na Musamman ga Maigirma Gwamnan Jihar Jigawa a Sabbin Kafafen Sadarwa)
10/10/2016

Sunday, 2 October 2016

DAN MAJALISA SANI ZORRO YA RABA TALLAFI GA JAMA'A. Daga Rabilu S. Kadeta...



Dan majalisar wakilai ta kasa mai wakilai kananan hukumomin Gumel da Maigatari da Suletankarkar da Maigatari Alhaji Muhammad Sani Zorro ya bada tallafin kayayyakin bunkasa tattalin arziki ga mata da maza 150 na mazabarsa.

Kayayyakin tallafin sun hadar da Babura da injunan markade da injunan wuta da kuma kekunan dinki yayinda mata hamsin suka sami tallafin wake da gero da kuma naira dubu uku kowannensu.

A jawabinsa wajen bikin, Alhaji Sani Zorro yace gwamna Badaru Abubakar yana bakin kokarinsa wajen ganin ancigaba da aikin tashar wutar lantarki ta garin Gagarawa.

A jawabinsa shugaban kwamitin riko na KH Gagarawa Alhaji Aminu Sule da shugaban APC na yankin Alhaji Mutari Kale sun bayyana cewar bada kayayyakin ya dace da manufar gwamna Badaru Abubakar na bunkasa tattalin arzikin maza da matan jihar nan

Wadanda suka sami tallafin Shafiu Ubale unguwar Liman da Hajara Liman Mutumbi sun yaba da wannan karamci

Rabilu S. Kadeta
P.R.O
Tsinkaya Social Network Gumel Chapter

Saturday, 1 October 2016

BIRTHDAY TO JIGAWA STATE GOVERNOR


Our Leader, Muhammad Badaru Abubakar @54. The Executive Governor of Jigawa State Alhaji Mohammed Badaru Abubakar who clocked 54, on Thursday (born 29 September 1962) was elected governor of Jigawa State in April 2015.  He is a member of the ruling All Progressives Congress Party (APC).

Early career...

Alhaji Mohammed Badaru Abubakar was born in the Babura Local Government Area of Jigawa State. He holds a Bachelor of Science (Hons) degree in Accountancy from the Ahmadu Bello University, and he is a Member of the National Institute (MNI). He also attended the National Institute for Policy and Strategic Studies (NIPSS) Kuru, Jos.
He served as an Auditor with the Audit Department of the Ministry of Finance and Economic Planning, Kano State, in 1987 and resigned in 1991 to establish his business outfit Talamiz Company. Talamiz Company was later incorporated as Talamiz Nigeria Limited, which later gave birth to subsidiaries such as Talamiz Motors, Talamiz Consumer Company, Talamiz Transport, Talamiz Commodities, Talamiz Properties, Talamiz Poultry and Farms, and Talamiz Petroleum.

He is also the Chairman of Talamiz Oil Mill Limited, Socar Talamiz Limited, RMR shipping Bv, AML Bonded Terminal, ALUAFRIC Cairo and a Director of Sahih Nigeria Limited.

He is a Recipient of National Honour of the Member of the Order of the Niger (MON) and Traditional Titles Holder of Sardauna of Ringim Emirate, and Wali of Jahun, all in Jigawa State.

Governor of Jigawa State Alhaji
Badaru Abubakar ran unsuccessfully for election on 26 April 2011. But lost to Sule Lamido who polled 676,307 votes, with runner-up Badaru Abubakar of the Action Congress of Nigeria (ACN) scoring 343,177 votes
In 2015 the Jigawa State All Progressives Congress (APC) governorship candidate, Alhaji Badaru Abubakar, was declared winner of the April 11 governorship election in the state. Announcing the results, Prof. James Ayatsa, said Alhaji Abubakar of APC scored 648,045 votes, while PDP candidate, Alhaji Aminu Ibrahim Ringim polled 479,447.

Our Wishes
As our Leader and Mentor clocked 54, our Governor is fondly remembered for the good leadership he has been providing and astonishing transformation that has taken place in Jigawa State despite the economic downturn. It is pleasing to acknowledge that since he assumed his present position, he has demonstrated uncommon dedication and commitment in the service to Jigawa State and our dear country, Nigeria.

Our wish and prayer is for the Almighty Allah to continue to strengthen him for more fruitful services to Jigawa State and Nigeria as a whole.

Once again, wishing His Excellency Happy Birthday and many happy returns!

Auwal D. Sankara,
S.A. Media.