Adsent

Thursday, 27 April 2023

LABARAI GOMA 10 A TAKAICE

 




1- Gwamnan jahar Ebonyi David Umahi ya yiwa wani sakataren dindindin (Permanent Secretary) jahar ritayar dole,Bayan da ya kasa lissafa adadin kudaden ma'aikatan da suka kammala aiki (Gratuity) 


2-  Kungiyar ' Yan tawayen dake rajin kafa kasar Biafra ta IPOB tace ZUNUFIN da Shugaba Buhari ya dauka akansu bazasu ta6a yafe Masa ba


3- Alh Atiku Abubakar ya yi ikirarin cewar yafi Cif Ahmed Bola Tinubu cancantar zama Shugaban Nageriya domin ba a Ta6a zarginsa da Ta'ammuli da Miyagun Kwayoyi ba


4- Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kaduna ta bawa iyalan tsohon Shugaban Kasar Nageriya Sani Abacha Nasara akan karar da suka shigar na Rushe Otel dinsu Mai suna ( Durbar Hotel) da Gwamnan jahar Malam Nasiru Elrufa'i yayi a Shekara ta 2020


5- Tsohon Gwamnan jahar Kano Injiniya Rabi'u Musa Kwankwaso ya ce zai zama mashawarci ga Za6a66an Gwamnan jahar Kano Abba Kabir Yusuf kuma yace za' tabbatar an gyara duk wata 6arnar da akayi da kuma kwato hakkin Al'ummar jahar  


6- Gwamnatin tarayya tace duk Shekara mutane kusan Miliyan 55 suke kamuwa da cutar zazzabin cizon sauro ( Malaria) kuma mutane dubu 90 ne ake bada ruhoton mutuwarsu sakamakon cutar


7- Shahararran Masoyin Nan na Shugaba Buhari kafin daga bisani ya zama makiyinsa wato Dan Bilki Kwamonda ya yi kaukausan suka akan Ministan sadarwar kasar Isa Ali Pantami inda ya ce Malamin baya Abu don Allah kuma Malami ne Dan FASHION


8- Kungiyar Masu gidajen Buredi ta( Bakers) tace sama da gidajen Buredi Dubu 26 aka rufe cikin Shekara 8 da Shugaba Buhari yayi yana Mulki


9- A wata takarda da Dakaceccen kwamonshinan zabe na jahar Adamawa Hudu Ari Yunusa ya akewa Rundunar'yan sanda da kuma ta farin Kaya SSS ya fadi sunayen wasu kwamanshinonin zabe 2 wato Abdullahi zuru da Baba Bila da cewar su suka taimaka Masa da Alkaluman boge domin ayi Magudi.


Menene Ra'ayin ka ki ko wani labari yafi Jan hankali?

Daga Usman Rangis.

Sunday, 19 March 2023

INEC DECLARED MALLAM UMAR NAMADI AS GOVERNOR.

 


The Independent National Electoral Commission (INEC) has declared the candidate of the All Progressives Congress (APC) in March 18 governorship poll in Jigawa State, Umar Namadi as the winner of the election.

The deputy governor and former commissioner of finance in the North-West state scored 618,449 votes to defeat his closest rivals — Mustafa Lamido of the Peoples Democratic Party (PDP) who polled 368,726 and Aminu Ringim of the New Nigeria People’s Party (NNPP) who got 37,156 votes.

Namadi will replace the incumbent, Abubakar Badaru of the APC whose two-term of eight years ends on May 29, 2023.

Saturday, 18 March 2023

ZABEN GWAMNA A JIGAWA..

 


Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa kuma Dan takarar gwamna Mallam Umar Namadi ya kada kuri'ar sa a mazabar sa, dake karamar hukumar Kafin Hausa. Da yake jawabi bayan kammala zaben ya bukaci jama'a da ayi zabe cikin lumana da kwanciyar hankali, ya kuma bukaci matasa da a kai zuciya nesa domin mai Nasara baya fada. 


Zabe dai a jihar jigawa ana yin sa cikin kwanciyar hankali da lumana, babu wani rahoto da ya nuna an samu rikici ko fasa Akwatin zabe. Tun farko dai jam'iyyar mai mulki a jihar wato Apc ta yi kira ga 'ya'yan ta da su guji duk wata fitina da zata kawo Tashin hankali ko janyo abinda zai kawo rashin zaman lafiya.