Adsent

Friday, 12 August 2016

JAJANTAWA GA AL'UMAR JIHAR JIGAWA...



Maigirma Gwamnan Jihar Jigawa Alhaji Muhammad Badaru Abubakar (MON, mni) yana jajantawa ɗaukacin al'umar Jihar Jigawa musamman al'ummomin Ƙananan Hukumomi da yankunan da ambaliyar ruwa ya masa ta'adi. 

Haƙiƙa wannan ibtila'i yana zuwa ne a daidai lokacin da Gwamnatin Jiha ta tashi haiƙan wajen ganin an kawo ƙarshen ire-iren waɗannan matsaloli na din-din-din, duba da irin hoɓɓasa da gwamnatin ke yi na samar da tituna da magudanan ruwa a duk faɗin Ƙananan Hukumomin Jihar. 

Duk da cewa Hukumar dake Harsashen Yanayi tace za'a samu Ambaliyar Ruwa a wasu Jihohi har da Jigawa, sannan Hukumar bada agajin gaggawa ta gargadi al'ummomin jihohin da ma wadanda suke makwaftaka dasu da suyi taka tsantsan, hakan ne yasa gwamnati ta tashi haiƙan don ganin an rage ƙarfin wannan matsaloli a gajeren zango da kawo ƙarshensu gaba ɗaya a dogon zango. 

Maigirma Gwamna ya bada umurni a kafa Kwamiti mai Ƙarfi da zai zagaya ya duba irin ɓarnar da ruwa yayi da nufin kawowa waɗanda abun ya shafa agaji na gaggawa. 

Maigirma Gwamnan yayi kira ga jama'a da su ƙara kula sosai wajen ganin an kare afkuwar hakan ta hanyar gyaran magudanan ruwa da yin cikon ƙasa a wuraren da ake buƙata, kuma ita ma a nata ɓangaren gwamnati zata shigo gadan-gadan don magance matsalar gaba ɗaya. 

A ƙarshe Maigirma Gwamnan yayi addu'ar Allah ya kare afkuwar hakan nan gaba, ya kuma maida alherin abinda aka rasa. 

Auwal D. Sankara, 
Mataimaki na Musamman ga Maigirma Gwamnan Jihar Jigawa a Sabbin Kafafen Sadarwa. 
12/08/2016

posted from Bloggeroid

Wednesday, 3 August 2016

GWAMNA MUHAMMAD BADARU YACE BA DON MUZGUNUWA WANI AKE TANTANCE MALAMAN MAKARANTUN FIRAMARE BA...




Maigirma Gwamnan Jihar Jigawa Alhaji Muhammad Badaru Abubakar (MON, mni) ya karbi bakuncin Shugabancin Gamayyar Kungiyoyin Matasan Jam'iyyar APC na Kananan Hukumomi 27 na Jihar Jigawa.
Kwamared Saleh Birniwa wanda ya jagoranci tawagar a matsayinsa na Shugaban Gamayyar Kungiyoyin yace sun kawo ziyarar ne domin taya Maigirma Gwamna murnar nasarar da ya samu a shekara guda da ya samu yana mulkin Jihar Jigawa, tare da jaddada goyon bayan su da hadin kansu ga Gwamnatin na Maigirma Gwamna.

Kwamared Birniwa ya yabawa irin matakan da ya dauke na tsantseni da sanya ido a dukiyar al'umar Jihar domin kai bantenta tsakanin takwarorinta, wanda shine dalilin da yasa Ma'aikatan Jihar ke samun albashinsu akan kari, tare da cigaba da ayyukan raya kasa, musamman ayyukan tituna da ake yi a fadin Jihar, wanda haka ne ma yasa ake kiran sa da "Baba Mai Kwakuleta".

Kwamared Saleh Birniwa yayi kuma kira ga Maigirma Gwamnan da ya duba irin hanyoyi da aka bi na daukan malaman makarantun firamare a gwamnatin da ta shude, duba da korafe korafen da aka samu, wanda ya janyo aikin da ake yi a halin yanzu na tantance Malaman bangaren. A karshe, Shugaban ya godewa Maigirma Gwamnan na fadada hanyoyin bunkasa tattalin arzikin Jihar da samar da kyakkyawan tsari ga masu zuba jari a cikin Jihar.

A jawabinsa, Maigirma Gwamna Muhammad Badaru Abubakar ya bayyana farin cikin sa ga wannan muhimmiyar ziyara da aka kawo masa, inda yace ziyarar na 'yan cikin gida ne wanda suke da ruwa da tsaki a samuwar gwamnatin.
Gwamna Badaru ya bayyana cewa Gwamnatin sa tana iya kokarinta na farfado da harkokin tattalin arzikin Jihar da kuma kulawa na musamman da take baiwa bangarorin Ilimi da na lafiya.
Gwamnan ya kara da cewa ayyukan tantance malaman makarantun firamare da ake yi a halin yanzu ba wai domin musguna wani ake yi ba, sai don karfafa bangaren.

A karshe Gwamna Muhammad Badaru ya yabawa musu da irin hakuri, juriya da fahimta da irin kokarin da suke yi na wayar da kan al'uma halin da gwamnati ta tsinci kanta a ciki na tabarbarewar tattalin arziki da kuma irin matakai da ake dauka na shawo kan lamuran, inda ya tabbatar musu da cewa matsalolin masu wucewa ne.

Rahoto daga Wakilin Tsinkaya a Gidan Gwamnati.

posted from Bloggeroid

GWAMNA MUHAMMAD BADARU YACE BA DON MUZGUNUWA WANI AKE TANTANCE MALAMAN MAKARANTUN FIRAMARE BA...




Maigirma Gwamnan Jihar Jigawa Alhaji Muhammad Badaru Abubakar (MON, mni) ya karbi bakuncin Shugabancin Gamayyar Kungiyoyin Matasan Jam'iyyar APC na Kananan Hukumomi 27 na Jihar Jigawa.
Kwamared Saleh Birniwa wanda ya jagoranci tawagar a matsayinsa na Shugaban Gamayyar Kungiyoyin yace sun kawo ziyarar ne domin taya Maigirma Gwamna murnar nasarar da ya samu a shekara guda da ya samu yana mulkin Jihar Jigawa, tare da jaddada goyon bayan su da hadin kansu ga Gwamnatin na Maigirma Gwamna.

Kwamared Birniwa ya yabawa irin matakan da ya dauke na tsantseni da sanya ido a dukiyar al'umar Jihar domin kai bantenta tsakanin takwarorinta, wanda shine dalilin da yasa Ma'aikatan Jihar ke samun albashinsu akan kari, tare da cigaba da ayyukan raya kasa, musamman ayyukan tituna da ake yi a fadin Jihar, wanda haka ne ma yasa ake kiran sa da "Baba Mai Kwakuleta".

Kwamared Saleh Birniwa yayi kuma kira ga Maigirma Gwamnan da ya duba irin hanyoyi da aka bi na daukan malaman makarantun firamare a gwamnatin da ta shude, duba da korafe korafen da aka samu, wanda ya janyo aikin da ake yi a halin yanzu na tantance Malaman bangaren.

A karshe, Shugaban ya godewa Maigirma Gwamnan na fadada hanyoyin bunkasa tattalin arzikin Jihar da samar da kyakkyawan tsari ga masu zuba jari a cikin Jihar.

A jawabinsa, Maigirma Gwamna Muhammad Badaru Abubakar ya bayyana farin cikin sa ga wannan muhimmiyar ziyara da aka kawo masa, inda yace ziyarar na 'yan cikin gida ne wanda suke da ruwa da tsaki a samuwar gwamnatin.
Gwamna Badaru ya bayyana cewa Gwamnatin sa tana iya kokarinta na farfado da harkokin tattalin arzikin Jihar da kuma kulawa na musamman da take baiwa bangarorin Ilimi da na lafiya.
Gwamnan ya kara da cewa ayyukan tantance malaman makarantun firamare da ake yi a halin yanzu ba wai domin musguna wani ake yi ba, sai don karfafa bangaren.

A karshe Gwamna Muhammad Badaru ya yabawa musu da irin hakuri, juriya da fahimta da irin kokarin da suke yi na wayar da kan al'uma halin da gwamnati ta tsinci kanta a ciki na tabarbarewar tattalin arziki da kuma irin matakai da ake dauka na shawo kan lamuran, inda ya tabbatar musu da cewa matsalolin masu wucewa ne.

RAHOTO DAGA WAKILIN TSINKAYA A GIDAN GWAMNATI.